Connect with us

Labarai

Abin da malaman kano suka faɗa kan ajiye aikin Daurawa

Published

on

Malaman Addinin Musulunci a Kano sun magantu kan murabus ɗin da Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Neptune Hausa ta rawaito a safiyar ranar Juma’a ce babban malamin ya sanar da sauka daga muƙamin a cikin wani saƙo na bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Sheikh Daurawa ya ɗauki matakin ne kwana guda bayan Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya soki Hukumar Hisbah bisa salon ayyukanta waɗanda ya ce suna keta doka.

Sheikh Daurawa ya ce gwiwoyinsa sun yi sanyi bayan da ya saurari kalaman gwamnan kan sukar da ya yi wa Hukumar Hisbah.

Sai dai a jawabin Sheikh Daurawa, ya bai wa gwamnan haƙuri sannan ya bayyana cewa ya sauka daga muƙaminsa.

“Mun yi iya ƙoƙarinmu, mu ga cewa muna abin da ya kamata, to amma ina ba mai girma gwamna hakuri bisa fushi da ya yi da maganganun da ya faɗa.

“Kuma ina rokon da ya yi min afuwa, na sauka daga wannan mukami da ya ba ni na Hisbah, inda muka yi kuskure muna fata a yafe mana. Kuma ina yi masa masa addu’a da fatan alheri.”

KU KUMA KARANTA: Da ɗumi-ɗumi: Aminu Daurawa ya sauka daga shugabancin Hisba a jihar Kano ( Bidiyo)

Sai dai kuma a wasu bidiyoyi da suka karaɗe soshiyal midiya, malaman da suka haɗa da Sheikh Abdallah Usman Gadon Kaya da Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo, sun bayyana rashin jin daɗinsu da kuma yadda suke ganin za a tari hanzarin lamarin.

A  bidiyon farko da Dokta Gadon Ƙaya ya fitar, ya yaba wa Gwamnan Kano kan ayyukan alherin da yake kawowa jihar, da kuma ƙoƙarinsa na karɓar gyara daga al’ummarsa.

Sai dai ya ce akwai buƙatar Gwamnan ya tausasa zuciyarsa ya zauna da Malam Daurawa, domin tattaunawa da shi ya kuma ba shi haƙuri.

“Muna ƙira ga gwamna Abba Yusuf da waɗanɗa ke kusa da shi su kai zuciya nesa su kira Malam Daurawa, su zauna da shi kuma su ba shi haƙuri kan abubuwan da suka faru.”

A cikin bidiyon, Sheikh Abdallah Gadon Ƙaya ya ce ya kamata Gwamna Abba Yusuf ya duba al’ummar Jihar Kano da ci gaban da Malam Daurawa ya kawo, baya ga gudummawar da yake bai wa ita kanta gwamnatin ta Kano.

“Ya kamata a zauna da shi Malam Daurawa a ba shi shawarwari a kan abubuwan ya yake yi ko ake ta cewa Hisbah take yi,” in ji Gadon Ƙaya.

“Matsayin Malam Daurawa ya kai kuma darajarsa ta kai.”

Kazalika, Gadon Ƙaya ya kuma bai wa Sheikh Daurawa haƙuri, da kuma roƙon ya amsa kiran Gwamna idan har ya buƙaci hakan, domin ci gaban jihar da kuma kukan da al’ummar jihar ke yi saboda ajiye aikinsa.

A nasa ɓangaren, Dokta Sani Umar Rijiyar Lemo kokawa ya yi da yadda Kano ta zama cibiyar yaɗa baɗala ta dandalin sada zumunta, da kuma yadda manyan jihar suka zuba ido ba tare da ɗaukar mataki ba.

Ya bayyana cewa, “ana nema a maida Kano dandalin baɗala, dandalin fasiƙanci da fajirci! Ana tasowa daga garuruwa masu nisa a zo cikinta domin a yi baɗala.

“Ba ma garuruwa ba, har ta kai yanzu daga ƙasashe maƙota ake ƙetarowa, yarinya ta baro iyayenta, ta shigo jihar, ta kama ɗaki da gida ta fara yaɗa baɗala.

“Tiktok ɗin nan yana yi a ko’ina in dai akwai network, amma ba su yarda su yi a ƙasarsu ba, ba su yarda su yi a cikin ’yan uwansu ba, saboda suna jin kunyar ’yan uwansu ko kuma ba za su ƙyale su ba, amma za su iya takowa su zo Kano su kama gida, su riƙa yin taswirar kanta cikin ƙazantacciyar shiga, da kalamai na batsa marasa kyau, suna antayo wa ’ya’yanmu.

“Ana ji ana gani ana sane da masu yin wannan abu amma an zuba musu ido. To idan ba a tashi tsaye ba aka taka musu burki aka yi abin da ya dace ba, babu shakka idan Allah Ya tashi kama mu da azaba, ba su kaɗai zai yi wa ba. Laifinmu shi ne ba mu yi wani abu ba,” inji shi.

Haka zalika, Sheikh Rijiyar Lemo ya jaddada cewa ƙoƙarin da Hisbah ke yi na umarni da kyakkyawa da yaƙi da baɗalar ne ɗaya daga cikin abubuwan da suka sanya ake samun sauƙi a jihar.

“Jiha ce da ta kowacce fuska za a cuta idan ɓarna ta shigo saboda yawan al’umma da dukiyar da ke ciki, amma Allah Ya tsare ta.”

Ya kuma ja hankalin gwamnati, da shugabanni, da sarakuna, haɗi da sauran malaman jihar kan illar zuba ido hakan ta ci gaba da faruwa, domin a cewarsa azabar da za ta game kowa ce a ƙarshe za ta faɗowa al’umma.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like