No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tattalin arziƙin Najeriya na ƙara haɓaka a ƙarƙashin mulkin Tinubu – Akume

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya bayyana kwarin gwiwa game da makomar Najeriya, yana mai cewa tattalin arzikin ƙasar na kara habaka a ƙarƙashin mulkin Shugaba Bola Tinubu.

Ya bayyana haka ne yayin bikin kaddamarwa da naɗin shugabanni na ƙungiyar Shugabannin Addinin Kirista na Arewacin Najeriya (NOCRELA), a Abuja a ranar Alhamis.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa taken taron shi ne: “Rawar da Shugabannin Kirista za su taka wajen Gina Ƙasa.”

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya janye dokar-ta-ɓaci a jihar Ribas, ya umarci Fubara ya dawo aiki

Akume ya ce bunƙasar da tattalin arziki daga kayan da ake ganewa a cikin kasa (GDP) da adadin ajiyar kuɗaɗen ƙasar na ƙasashen waje (foreign reserves) na samun ci gaba. A cewarsa, GDP ya kara habaka da kashi 4.4%, kuma ajiyar kuɗin waje ta kai dala biliyan 42.

Ya kuma yi kira da a samu haɗin kai tsakanin ‘yan Najeriya, yana jaddada yadda Shugaba Tinubu ke iya aiki tare da mutane masu addinai da ra’ayoyi daban-daban.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...