Za a dinga koyar da yaren China a makaratun Sakandire na Najeriya – Gwamnatin Tarayya 

0
140
Za a dinga koyar da yaren China a makaratun Sakandire na Najeriya - Gwamnatin Tarayya 
Sakataren Ilimi, Dakta Danlami Hayyo

Za a dinga koyar da yaren China a makaratun Sakandire na Najeriya – Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da saka harshen China (Mandarin) a cikin kundin karatun makarantun sakandare a Najeriya.

Sakataren Ilimi na Abuja, Dakta Danlami Hayyo ne ya bayyana hakan a Abuja yayin kaddamar da “Chinese Corner” na 14, inda ya ce wannan mataki na nuna muhimmancin harshen Mandarin a kasuwanci, ilimi, al’adu da diflomasiyya.

Ya ce koyar da ɗalibai harshen zai ba su damar gogayya a duniya tare da samun damar ilimi da kasuwanci.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Yobe ta haramta bukukuwan ‘Marker Day’ a dukkan makarantun Sakandire, saboda lalata tarbiyya

A cewarsa, wannan shiri wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati wajen shirya matasa domin zama masu iya yin gogayya a fagen duniya.

Ana ganin matakin zai kara zurfafa dangantakar Najeriya da ƙasar China a fannoni da dama, musamman ilimi da musayar al’adu.

Leave a Reply