No menu items!

Sample Page Title

Date:

APC a Kano ta buƙaci hukumar INEC ta soke zaɓen cike gurbi na Shanono/Ɓagwai

Daga Jameel Lawan Yakasai

Jam’iyyar APC ta roƙi Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) da ta soke zaɓen cike gurbi na mazabar Shanono/Bagwai da kuma karasa zaɓen Ghari da aka gudanar a jihar Kano.

Wannan na cikin sanarwar da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Felix Morka, ya fitar ranar Asabar a Abuja.

APC ta ce zaɓen bai dace da ka’idojin gaskiya da adalci ba saboda tashin hankali da kuma rikicin da ya mamaye wuraren kada kuri’a.

KU KUMA KARANTA: Zaɓen cike gurbi a Kano: An kama ‘yan daba sama da 100 da ake zargi da yunƙurin tayar da tarzoma – INEC

Jam’iyyar ta bayyana cewa rahotanni daga Shanono, Bagwai da Ghari sun nuna cewa jama’a sun tsere daga rumfunan zaɓe, yayin da jami’an tsaro suka kasa shawo kan ‘yan daba da ke tayar da hankali.

Sanarwar ta ƙara da cewa ci gaba da gudanar da wannan zaɓe a irin wannan yanayi zai zama tamkar yi wa dimokuraɗiyya fyade tare da fito da sabuwar mummunar hanya ta tafka maguɗi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...