No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya fice daga PDP

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, GCON, ya fice daga jam’iyyar PDP a hukumance ba tare da ɓata lokaci ba, saboda “bambance-bambancen da ba a daidaita ba” da yadda jam’iyyar ke tafiya a halin yanzu. Inji shi.

A wata takarda mai ɗauke da kwanan watan 14 ga watan Yuli, 2025, ga shugaban jam’iyyar PDP, Jada 1 Ward, Jada LGA, jihar Adamawa, Atiku ya bayyana matuƙar jin daɗinsa kan damammakin da jam’iyyar ta ba shi.

KU KUMA KARANTA: Haɗakar Atiku, El-Rufa’i da Obi ba zai iya kayar da APC ba a 2027 – Shekarau

Yin hidimar cikakken wa’adi biyu a matsayin mataimakin shugaban Najeriya da zama ɗan takarar shugaban ƙasa sau biyu yana ɗaya daga cikin abubuwa muhimmai a rayuwata,” ya rubuta a takardar.

Atiku, wanda yana cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar PDP, ya bayyana yin murabus ɗinsa a matsayin abin takaici. Duk da haka, ya ce, “Na ga ya zama dole in raba hanya saboda yanayin da Jam’iyyar ta ɗauka a halin yanzu, wanda na yi imanin ya bambanta da ƙa’idojin da muka tsaya a kai.”

Ya ƙara da cewa, “Da baƙin ciki ne na yi murabus, tare da fahimtar bambance-bambancen da ba a daidaita su ba da suka kunno kai.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi fatan alheri ga jam’iyyar da shugabanninta a nan gaba. Shugaban jam’iyyar na yankin ya karɓi takardar kuma ya amince da shi a wannan rana.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...