No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za mu ci gaba da karya farashin shinkafa – Abdulsamad BUA

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya yi alƙawarin kara rage farashin shinkafa da sauran kayayyakin abinci, wanda ya ce tuni ya ragu a shekarar da ta gabata.

Ya yaba wa shugaban kasa Bola Tinubu bisa yadda ya bayar da dama wajen shigo da wasu nau’ikan abinci daga waje, yana mai cewa hangen nesan shugaban ya taimaka wajen faduwar farashin kayan abinci a kasar nan.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Kano da haɗin gwiwar ‘yan kasuwa sun rage farashin kayan abinci

Da yake zantawa da manema labarai a fadar gwamnatin tarayya bayan ganawarsa da Tinubu a ranar Alhamis, Rabiu ya ce kamfanin BUA ya yi amfani da damar da a ka bayar wajen shigo da nau’ikan samfarerar alkama, masara da shinkafa mai yawa.

Ya ce kungiyar manoman shinkafa sun hadar kai domin magance matsalar boye kaya da wasu kamfanoni ke yi, ya ce kungiyar ba za ta bari wani daga cikin ‘ya’yanta ya boye shinkafa ba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...