No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yansanda ta hana hawan Sallah a Kano

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Rundunar ƴansanda ta jihar Kano ta hana hawan sallah a lokacin bukukuwan Ƙaramar Sallah saboda dalilan tsaro da kuma bukatar tabbatar da zaman lafiya.

Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori ne ya sanar da hakan yayin ganawa da manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Bompai a yau Juma’a.

CP Bakori ya jaddada muhimmancin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a lokacin bukukuwan.

KU KUMA KARANTA:Mun janye bukin hawan sallah, domin zaman lafiya – Sarki Aminu Ado Bayero

A cewarsa, bayanan sirri da aka samu sun nuna akwai barazana ta tashin hankali da ke tattare da hawan, wanda zai iya haifar da tarzoma.

“Bayan sahihin rahotannin sirri na tsare-tsare da ’yan bata-gari da masu daukar nauyinsu suka shirya na amfani da bawan sallah wajen kawo tarnaki, rundunar ‘yan sandan tare da tuntubar gwamnatin jihar Kano da sauran masu ruwa da tsaki, ta yanke shawarar haramta duk wani abu na hawa a fadin jihar,” in ji CP Bakori.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...