No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ta’addancin ’yan bindiga ya ragu da kashi 70 a Katsina — Dikko Raɗɗa

Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Raɗɗa, ya ce gwamnatinsa ta yi nasarar rage ta’addancin ’yan bindiga da kashi 70 cikin ɗari a cikin shekara ɗaya da ta gabata.

Gwamnan ya ce an samu wannan nasara ne a sakamakon abin da ya kira kyakkyawan hadin kai tsakanin jami’an tsaro na sa-kai na jihar da kuma jami’an tsaro na ƙasar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa gwamnan ya faɗi hakan ne yayin wata hira da manema labarai a Yola babban birnin Jihar Adamawa, a jiya Asabar.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Raɗɗa ya biya kuɗin Hadaya ga dukkanin alhazan Katsina

Gwamnan wanda ya kai ziyarar aiki birnin Yola, ya ce lokaci ya yi da ya kamata a samu ‘yan sandan jihohi da za a sanya su shiga yaƙin da ake yi da matsalar tsaro a ƙasar.

Gwamna Radda, wanda ya ce sun bullo da dabarar yakar barayin, ya kara bayani da cewa abin da ake gani yanzu ‘yan bindigar na kai hari ne a kauyuka da yankunan da suke surkuki, inda suke kona gidaje da kashe jama’a.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...