No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Muhammad Shehu Dalijan, a madadin Sufeto Janar na ‘yansandan IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya gabatar da cek ɗin naira miliyan hamsin da dubu ɗari da arba’in da biyar, da naira ɗari da goma sha tara da kobo tamanin da uku (50,145,119.83) ga ’yan’uwa 27 na jami’an ‘yansanda da suka mutu a lokacin da suke bakin aikin su.

Waɗannan cak da aka bayar wani ɓangare ne na shirin IGP a ƙarƙashin tsarin inshorar jin daɗin iyali na ƙungiyar da IGP don taimaka wa iyalan jami’an mu da ke biyan fansho mai tsoka a lokacin da suke raye.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ASP Yazid Abubakar, ya ce CP, ya bayyana haka a takardar ya sa hanu ga manema labarai a Gusau.

KU KUMA KARANTA: Rashin tsaro: Gwamnoni 16 na goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi

A cewar sa SP Yazid, ya yabawa IGP bisa wannan karamcin da ya nuna, sannan ya kuma yi ƙira ga iyalan jami’an da suka rasu da su yi amfani da kuɗin da kyau da kuma kula da iyalansu.

Malam Yahaya Umar ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin a jawabinsa a madadin sauran waɗanda suka amfana, ya gode wa babban sufeton ‘yansanda da rundunar ‘yansandan jihar bisa wannan tallafi.

Ya kuma ba da tabbacin cewa za a kashe kuɗaɗen da aka ba su ta hanyar da ta dace.

Yayi fatan samun zaman lafiya a jihar Zamfara da Najeriya baki ɗaya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...