Connect with us

Labarai

Za a gurfanar da mutanen da ake zargi da rajin kafa ƙasar Yarbawa a kotu – Ƴan sanda

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Oyo da ke kudancin Najeriya ta ce nan gaba kaɗan za ta gurfanar da mutanen da ta kama bisa zargin fafutukar kafa ƙasar Yarbawa a gaban kotu.

A ranar Asabar da ta wuce ne, ƴan sanda suka kama ƴan kungiyar bayan mamayar da suka yi wa Ofishin gwamnar jihar Oyo da kuma majalisar dokokin jihar suna sanye da kakin soji kuma riƙe makamai daban-daban da kuma tutar ƙasar da suke son kafawa.

Kazalika rahotanni sun ce mutanen sun yi yunƙurin kutsa kai cikin ofishin gwamnan jihar, amma jami’an tsaro su fatattake su tare da kama da dama daga cikinsu.

Ana zargin matar hamshakin ɗan kasuwa kuma fitaccen ɗan siyasa, marigayi Cif Moshood Abiola, mai suna Dupe Onitiri- Abiola da ɗaukar nauyin masu fafutukar bayan wani bidiyo da ta wallafa wanda ya karaɗe shafukan intanet, tana mai iƙirarin ɓallewa daga Najeriya da kuma kafa shugabancin ƙasa ga al’ummar Yarbawa.

KU KUMA KARANTA: Rashin tsaro: Gwamnoni 16 na goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Oyo, Hamzat Adebola, ya bayyana lamarin a matsayin laifi da rashin kishi da cin amanar ƙasa da kuma ayyukan ta’addanci a yayin da yake gabatar da mutanen da ake zargi a gaban ‘yan jarida, yana mai cewa ”za a hukunta su bisa tanadin doka.”

“Da farko ƴan sanda sun gargaɗi masu fafutukar da su watse amma sai suka yi kunnen-ƙashi daga nan gangaminsu ya juya zuwa rikici sai suka buɗe wuta kan ‘yan sanda da kuma tawagar jami’an sa-kai na Amotekun da ke wurin,” a cewar kwamishinan.

”An ƙwato bindigogi masu sarrafa kansu guda biyar da wasu tarin makamai da kayan sojoji guda 72 da harsashai 405 da dai sauransu,” in ji Kwamishinan ƴan sandan.

Haka kuma jaridun Najeriya sun ruwaito cewa ƴan sandan jihar Oyo na neman Onitiri-Abiola ruwa-a-jallo, sai dai a yayin jawabin Kwamishinan bai ambaci sunanta ba amma mai bai wa Gwamnan Jihar Oyo shawara kan harkokin tsaro Mista Fatai Owoseni ya ce ana sane da cewa ita ce take jagorantar ƙungiyar ta masu rajin kafa ƙasar Yarbawa daga Najeriya.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Oyo ya ce rundunar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da haɗin kan Najeriya.

“Ina so na yi amfani da wannan dama wajen tunatar da masu aikata laifuka cewa jihar Oyo jiha mai karɓar baki da kuma haziƙan mutane waɗanda ke alfahari da kansu a fannin ƙirƙire-ƙirƙire, da kuma aiki tuƙuru da wadata,” in ji shi.

Wasu daga cikin waɗanda aka kama sun shaida wa manema labarai cewa ba su yi nadamar mamayar da suka yi wa Ofishin gwamnatin jihar ba.

Sun ce sun bi matakai da suka kamata kuma ba su ci amanar ƙasa ba. “Ba mu yi nadama ba, mun bi tsarin da ya kamata mu bi,” kamar yadda suka shaida wa manena labarai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Published

on

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

An jiyo Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja yana ba da umarnin jami’an tsaronsa da su yi wa wani malamin addinin Islama cin mutunci a yayin bikin addu’ar Fidda’u ga matar mataimakinsa, Hajiya Zainab Yakubu Garba da ta rasu.

Lamarin wanda ya auku a Minna a ranar Juma’a, ya auku ne a lokacin da malamin ya sadaukar da kansa domin gudanar da addu’a, lamarin da aka ce ya harzuƙa Gwamna Bago.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin Gwamna Bago yana jawabi ga masu jajantawa, inda ya nuna cewa za a iya gudanar da addu’o’i ga marigayiyar a cikin gida, kafin daga bisani ya fusata a lokacin da malamin ya fito.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Ya tuhumi malamin, sannan ya umurci jami’an tsaronsa da su ɗauki mataki, inda ya umarce su da su yi masa mari mai kyau sannan su kama shi.

Shaidu da suka halarci taron sun nuna kaɗuwa dangane da wannan hali na gwamnan, inda suka yi la’akari da irin tsaurin ra’ayinsa ga malamin.

Wannan lamari dai ya ƙara rura wutar zarge-zargen da ke tattare da yadda Gwamna Bago ke da alaƙa da cin zarafi ga mataimaka da magoya bayansa, kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito kuma majiyar gwamnan ta tabbatar.

Kalli bidiyon a nan:

Continue Reading

Labarai

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Published

on

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Ministocin kuɗi da Gwamnonin manyan Bankunan ƙasashen ƙungiyar raya tattalin arzikin Yammacin Afirka 15, sun ci gaba da shirye-shiryen ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da aka yiwa laƙabi da ECO.

Wannan yunƙuri da ke da nufin haɓaka tattalin arziƙi yankin Afirka ta Yamma, ya samu amincewar tarayyar Najeriya.

A wata sanarwa da ma’aikatar kuɗi ta Najeriyar ta fitar jiya juma’a, ɗauke da sa hannun Daraktan watsa Labarai, Mohammed Manga, ta ce Ministan Kuɗin ƙasar Wale Edun, ya lura da muhimmiyar rawar da kuɗin na bai ɗaya zai taka wajen bunƙasa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ci gaban yankin baki ɗaya.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Edun, ya kuma jaddada ƙudirin Najeriya na ci gaba da shiga gaba wajen aiwatar da shi, wanda ake ganin wani ɓangare ne daga shirin hukumar yin katin ɗan ƙasa na samar da kati guda mai amfani a wurare uku, wanda ake sa ran zai fara aiki a watan Agusta mai zuwa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like