No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an tsaron Najeriya sun kama biyu daga cikin shugabannin manhajar hada-hadar kuɗin kirifto wato Binance a wani samame da suka kai musu, a cewar jaridar the Financial Times, wadda ta ambato wasu majiyoyi da ke da masaniya game da batun ranar Laraba.

Shugabannin Binance ɗin sun je Najeriya ne sakamakon matakin da gwamnatin ƙasar ta ɗauka na rufe manhajar a ƙasar a makon jiya, sai dai nan-take ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan sha’anin tsaro ya bayar da umarnin tsare su, in ji rahotanni.

Masu manjahar ta Binance ba su ce komai ba game da kama shugabannin nasu, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.

A makon jiya gwamnatin Najeriya ta zargi Binance da taka muhimmiyar rawa wajen tashin farashin dala a ƙasar da kuma lalacewar darajar naira abin da ya jefa tattalin arzikin ƙasar cikin mawuyacin hali.

Wata majiya daga Hukumar Kula da Sadarwa ta Najeriya NCC ta tabbatarwa TRT Afrika Hausa cewa an bai wa kamfanoni na waya umarnin ɗaukar matakin, kuma har ma an fara aiki da shi, musamman ga masu amfani da waya.

KU KUMA KARANTA: CBN ya janye haramcin amfani da kuɗaɗen Kiripto

Ranar Talatar da ta wuce, gwamnan Babban Bankin Najeriya, CBN, Olayemi Cardoso, ya ce wasu mutane da ba su sani ba “sun yi hada-hadar dala biliyan 26 ta manhajar Binance a Najeriya a cikin shekara ɗaya da ta wuce”.

Ya ƙara da cewa hakan yana barazana ga tattalin arziki da tsaron Najeriya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...