Connect with us

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe basarake, sun yi tafi da matarsa a Kwara

Published

on

Daga Maryam umar Abdullahi

Wasu mutane ɗauke da makamai sun harbe wani basaraken gargajiya, tare da yin garkuwa da matarsa da kuma wani mutum guda a yankin arewa maso tsakiyan Najeriya, kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Maharan dai sun kai farmaki ne a fadar Segun Aremu, janar ɗin soja mai ritaya kuma basarake mai suna Olukoro na Koro a daren ranar Alhamis.

Ba a dai bayyana ko su waye ‘yan bindigar ba ko kuma masu neman kuɗin fansa ne ko kuma a’a.

KU KUMA KARANTA:Masu gurasa sun yi zanga-zanga kan tsadar fulawa a Kano

Wannan sabon kisa da sace mutane ya zo ne kwanaki bayan masu fafutuka sun buƙaci a kafa dokar ta ɓaci domin shawo kan lamarin.

Wasu ƙungiyoyin farar hula 50 ne ke son shugaba Bola Tinubu ya yi wannan iƙirarin, inda aka ce sama da mutane 1,800 aka sace tun bayan hawansa mulki a watan Mayun da ya gabata.

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da yake yin Allah wadai da kisan da aka yi wa Olukoro na Koro a jihar Kwara, a matsayin “rashin hankali, mai ban tsoro, kuma abin ƙyama”, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya sha alwashin kama waɗanda suka aikata wannan laifin. ‘Yan sanda kuma sun ce ana farautar mutanen.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Published

on

'Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Wata ƙungiya ɗauke da makamai ta kai hari a yayin wani bikin aure a tsakiyar ƙasar Mali tare da kashe aƙalla mutane 21, kamar yadda mazauna yankin suka faɗa a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin sojojin ƙasar Afirka ta Yamma ke fafutukar yaƙi da tashe-tashen hankula daga masu tsattsauran ra’ayi.

Maharan sun kutsa ƙauyen Djiguibombo akan babura wanda ke garin Bandiagara a yammacin ranar Litinin ɗin da ta gabata yayin da mazauna yankin ke bikin ma’auratan, a cewar Bakary Guindo, shugaban ƙungiyar matasan yankin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

“Yawancin waɗanda abin ya shafa yankan rago aka musu” in ji Guindo.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai ya biyo bayan irin wanda ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta JNIM da ke da alaƙa da Al-Qaida ke kai hare-hare a yankin.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like