No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya gana da shugaban ɓangaren siyasa na ƙungiyar Hamas, Ismail Haniyeh, a cewar wasu majiyoyi na diflomasiyyar Turkiyya.

Fidan and Haniyeh sun tattauna ranar Asabar kan batun tsagaita wuta nan-take a Gaza da kai ƙarin kayan agaji yankin da sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma samar da ƙasashe biyu masu ‘yancin kansu.

Hare-haren da Isra’ila take kai wa a Gaza sun raba kashi 85 na mutanen yankin da muhallansu a yayin da ake cikin tsananin rashin abinci da ruwa mai tsafta da magunguna, sannan an rusa kashi 60 na gine-ginen yankin, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

A watan Oktoban da ya wuce, Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya tattauna da Haniyeh bayan Isra’ila ta kaddamar da hare-hare a Gaza inda ya tabbatar masa cewa Ankara zai kai kayan agaji Gaza sannan za a ɗauko waɗanda suka jikkata a yankin domin kawo su Turkiyya su yi jinya idan akwai buƙatar hakan.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe farar hula bakwai a Gaza da Khan Younis

Shugaba Erdogan ya jaddada cewa ba za a samu dauwamammen zaman lafiya a yankin ba sai Falasɗinawa sun samu kasa mai zaman kanta kamar yadda take a 1967 wacce Birnin Kudus zai zama babban birninta.

Erdogan ya ƙara da cewa Turkiyya za ta ci gaba da fafutuka domin ganin an samu zaman lafiya a yankin.

Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare babu kakkautawa ta sama da ta ƙasa a Gaza tun bayan da Hamas ta kai mata barin ba-zata, wanda Tel Aviv ya ce ya kashe aƙalla mutum 1,200.

Ta kashe Falasɗinawa aƙalla 24,927, galibinsu mata da ƙananan yara, sannan an jikkata mutum 62,388, a cewar hukumar lafiya ta Falasɗinu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...