No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar tara haraji ta jihar Kano (KIRS) ta sanar da korar daraktoci 8 daga muƙamansu, inda ta umarce su da su miƙa duk wani aiki da muƙamai ga mataimakan su.

Shugaban hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta jihar Kano (KIRS), Alhaji Sani Abdulkadir Dambo ne ya sanar da hakan a wata sanarwa daga ofishin sa.

Ya ƙara da cewa, “A ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na cimma manufofin gwamnati mai ci, an umurce ni da in sanar da ku cewa an sauke daraktocin, kuma za su miƙa takardun aikinsu ga mataimakansu nan take.

KU KUMA KARANTA: An kori ‘yan sanda biyu daga aiki bayan samun su da yin fashi da makami

A cewar sanarwar, daraktocin sassan da abin ya shafa sun haɗa da: Darakta Muhammad Kabir Umar; Daraktan Ma’aikata, Kabiru Magaji; Daraktan Kasuwanci Ibrahim Sammani; Aminu Umar Kawu, Daraktan Muhd Auwal Abdullahi, Daraktan Binciken Haraji

Ta ƙara da cewa sauran daraktoci sun haɗa da Abubakar Garba Yusuf, Daraktan ICT, Hamisu Ado Magaji, Daraktan PAYE, da Bashir Yusuf Madobi, Daraktan Legal & Enforcement.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...