Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta yi bayani kan dalilan rufe kasuwannin dabbobi

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana dalilin rufe wasu kasuwannin dabbobi a jihar.

Alfijir labarai ta rawaito a ranar Laraba ne gwamnatin jihar ta sanar da rufe kasuwannin a ƙananan hukumomi bakwai waɗanda ta ce ana hada-hadar shanu da dabbobin sata.

Mannir Haidara Kaura, kwamishinan watsa labarai da raya al’adu na jihar, ya bayyana wa BBC Hausa cewa an ɗauki wannan mataki ne a wani yunƙuri na tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin jama’ar jihar.

Ya ce bayanan da gwamnati da hukumomin tsaro suka samu sun nuna cewa ‘yan fashin daji na shigo da dabbobin da suka ƙwace a hannun mutane suna cinikinsu inda suke samun kuɗin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga a Taraba sun sace mutane ana tsaka da cin kasuwa

Yanayi na tsaro abu ne da ke da sarƙaƙiya, amma dai muna ganin matakan da wannan gwamnati ke ɗauka za su fara tasiri ba da jimawa ba, domin za mu toshe musu wannan kofa” in ji kakakin gwamnatin

Ba dai wannan ne karon farko da gwamnatin jihar ta Zamfara ke rufe kasuwannin dabbobi ba, bisa zargin hada-hadar dabbobin sata da ‘yan fashin daji ke kawowa.

A watan Satumba ma akwai wasu kasuwanni guda bakwai da gwamnatin jihar ta rufe saboda irin wannan zargi, inda ake ci gaba da bincike.

Jihar Zamfara dai na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar tsaro a Najeriya, inda yan fashin daji ke kai hare-hare, suna kashe jama’a da kuma satar dukiyoyinsu, ciki har da dabbobi.

Sai dai gwamnatin jihar na ganin cewa irin waɗannan matakai da take ɗauka, za su taimaka wajen shawo kan matsalar da ta ki ci ta ki cinyewa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like