Connect with us

Kasashen Waje

Girgizar ƙasa ta kashe sama da mutane 100 a arewa maso yammacin China

Published

on

Aƙalla mutane 116 ne suka mutu sakamakon girgizar ƙasar da ta ruguje gidaje a arewa maso yammacin ƙasar China, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na ƙasar suka ruwaito da safiyar Talatan nan, yayin da jami’an ceto suka dukufa wajen tona baraguzan gine-gine cikin wani yanayi mai sanyin gaske.

Jami’ai a lardin Gansu da lamarin yafi muni sun ce kimanin mutane 105 ne suka mutu sannan kusan 400 suka jikkata, sakamakon girgizar ƙasa mai karfin gaske da ta afku da tsakar dare.

Gidan talabijin na ƙasar CCTV, ya ruwaito cewar, a can birnin Haidong na lardin Qinghai mai makwabtaka kuwa girgizar ƙasa ta kashe mutane 11 tare da jikkata wasu 100.

KU KUMA KARANTA: An yi girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 3.6 a Ghana

Kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya bayyana cewa, girgizar ƙasar mai karfin maki 5.9 ta yi ɓarna sosai, da suka haɗa da rugujewar gidaje, tare da warwatsa bin titi domin neman tsira.

An fara aikin ceto da sanyin safiyar Talata, inda shugaban ƙasar Xi Jinping ya yi ƙira da aƙara azama a aikin ceto da kuma tabbatar da tsaron waɗanda suka tsira da kuma dukiyoyinsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Published

on

Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Hukumomin sojan Nijar, Mali da Burkina Faso sun yi bikin raba gari da sauran ƙasashen yammacin Afirka a ranar Asabar, yayin da suka rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya ta kafa wata ƙungiya a tsakaninsu.

Taron farko na ƙasashen uku, waɗanda dukkaninsu suka fice daga ƙungiyar ECOWAS a farkon wannan shekarar, an kuma buƙaci a ƙara yin haɗin gwiwa a ɓangarori da dama.

“Mutanenmu sun juya baya ga ƙungiyar ECOWAS ba tare da wata tangarɗa ba,” in ji Janar Abdourahamane Tiani mai mulkin Jamhuriyar Nijar, ya shaidawa ‘yan’uwansa masu faɗa a ji a yankin Sahel a wajen buɗe taron da aka yi a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Shugabannin ukun da suka karɓi mulki ta hanyar juyin mulki a shekarun baya-bayan nan, sun yanke shawarar ɗaukar wani mataki na ƙara samun haɗin kai, tare da amincewa da yarjejeniyar kafa ƙungiyar, a wata sanarwa da suka fitar a ƙarshen taron.

Ƙungiyar ƙasashen yankin Sahel da za ta yi amfani da sunan AES kuma za ta kasance ƙarƙashin jagorancin ƙasar Mali a shekara ta farko, adadin ya kai kimanin mutane miliyan 72.

Continue Reading

Kasashen Waje

Shugabannin ƙasashen ƙungiyar AES sahel za su gudanar da taron ƙoli a Yamai

Published

on

Shugabannin ƙasashen ƙungiyar AES sahel za su gudanar da taron ƙoli a Yamai

Shugabannin ƙasashen ƙungiyar AES sahel za su gudanar da taron ƙoli a Yamai

 

Shugabanin gwamnatocin mulkin sojan Burkina Faso, Mali da Nijar na shirin gudanar da taronsu na farko a ƙarƙashin inuwar ƙungiyar AES a ranar Asabar 6 ga watan Yuli a birnin Yamai.

Taron dai na da nufin jaddada haɗin kan da ke tsakanin ƙasashen uku ne bayan da a watan Janairun da ya gabata suka fice daga ƙungiyar ECOWAS.

Waɗannan ƙasashe na fama da aika-aikar kungiyoyin ta’addanci saboda haka babbar maganar kuɗaɗen bai ɗaya taron zai tattauna hanyoyin da za’a tunkari wannan lamari da ke haddasa kisan ɗimbim jami’an tsaro da fararen hula.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Sanarwar fadar shugaban majalissar CNSP na cewa kaftin Ibrahim Traore na Burkina Faso da Kanal Assimi Goita na Mali zasu sauka birnin Yamai da la’asariyar ranar Juma’a a albarkacin taron ƙoli na farko na shugabanin ƙasashen AES da zai gudana a ranar asabar.

Tare da mai masauƙin baƙi Janar Abdourahamane Tiani na Nijar waɗannan shugabanin gwamnatocin mulkin soja za su tattauna akan matsalolin da ke addabar ƙasashen uku.

A watan Fabrairun da ya gabata ne ministoci daga ƙasashen Mali, Nijar da Burkina Faso a ƙarshen taron da suka gudanar a Ougadougou suka shawarci shugabanin ƙasashen su yi nasu taron don jaddada abubuwan da suka tsayar mafarin wannan haɗuwa ta Yamai da zai kasance lokaci na saka hannu kan takardun tabbatuwar haɗin kai ta yadda za su kasance masu manufofi guda. Abin da Mahamadou Tchiroma AIssami jigo a ƙungiyar ROTAB ya ƙira ci gaba a ƙoƙarin ‘yantar da yankin Sahel.

Batun kuɗaɗen bai ɗaya na kasashen Sahel na daga cikin abubuwan da waɗannan shugabanni za su tsaida magana a kansu kasancewarsa ɗaya daga cikin igiyoyin da ake zargin Faransa na ci gaba da amfani da su don jan zarenta a wajen kasashen da ta yi wa mulkin mallaka.

Nijar, Mali da Burkina Faso sun faɗa ƙarƙashin mulkin soja sakamakon lalacewar al’amuran tsaro inda ƙungiyoyin ta’addanci ke yaɗa ayyukan da ake zargin ƙasashen yammaci da hannu wajen kitsawa.

Ƙasashen uku dai sun fice daga CEDEAO a watan Janairun 2024 saboda zargin shugabaninta da kaucewa manufofin kungiyar. Sannan sun kafa rundunar haɗin guiwar AES a watan maris ɗin da ya gabata da zummar tunkatar ƙalubalen tsaron da ke haddasa mutuwar sojoji da fararen hula a kowacce daga cikinsu.

Continue Reading

Kasashen Waje

Amurka za ta kammala janye sojojinta daga Nijar ranar Lahadi

Published

on

Amurka za ta kammala janye sojojinta daga Nijar ranar Lahadi

 

Amurka za ta kammala janye sojojinta daga Nijar ranar Lahadi

A ranar Lahadi ne Amurka za ta kammala janye dakarunta da kayan aikinta daga sansanin sojin sama da ke Yamai babban birnin ƙasar Nijar a yammacin Afirka, tare da gudanar da bikin janyewar.

Mataki na gaba a ajandar Amurka shi ne ficewarta daga wani sansanin jiragen yaƙi marasa matuƙi na Nijar, wanda aka shirya kammala shi a watan Agusta.

Ficewar dai ya yi daidai da wa’adin ranar 15 ga watan Satumba da hukumomin Amurka da na Nijar suka amince da shi, bayan da sabbin shugabannin sojojin Nijar suka umarci sojojin Amurka da su fice bayan juyin mulkin da aka yi a Yamai a bara.

KU KUMA KARANTA:Sojojin Amurka za su kammala ficewa daga Nijar 15 ga Satumba

Babban hafsan sojin saman Amurka, Manjo Janar Kenneth Ekman, ya na Nijar domin daidaita hanyoyin fita, ya shaidawa manema labarai ta hoton bidiyo cewa za a mayar da yawancin sojojin Amurka da ke Nijar zuwa ƙasashen Turai. Sai dai ya ce an mayar da ƙananan tawagogin sojojin Amurka zuwa wasu ƙasashen yammacin Afirka.

Yayin da Amurka ta janye wasu muhimman kayan aiki daga sansanonin a Nijar, ba ta lalata kayan aiki da kayayyakin da za a bari a baya ba. Da yake nuna fara mai kyau nan gaba, Ekman ya ce, “Manufarmu a cikin aiwatar da hukuncin shi ne, a bar abubuwa cikin yanayi mai kyau gwargwadon iko. Ya ƙara cewa “Idan muka fita muka bar ta cikin rugujewa, ko kuma muka fita ta rashin mutunci, ko kuma idan muka lalata abubuwa kamar yadda muka tafi, za mu hana zaɓin da ƙasashen biyu ke buƙata na gaba. Kuma har yanzu manufofinmu na tsaro suna cikin ruɗani.”

Janjewar musamman daga sansanin jirage marasa matuƙi wani rauni ne ga Amurka da ayyukanta na yaƙi da ta’addanci a yankin Sahel, babban yankin Afirka, inda masu tada ƙayar baya, masu alaƙa da al-Qaida da ƙungiyoyin IS ke gudanar da ayyukansu.

Ekman, wanda shi ne daraktan dabarun yaƙi na rundunar sojojin Amurka a Afirka, ya ce sauran ƙasashen Afirka da ke cikin damuwa game da barazanar ‘yan tada ƙayar baya da ke yankin Sahel, sun tunkari Amurka kan yadda za su haɗa kai da sojojin Amurka domin yaƙar ‘yan ta’adda. “Nijar ta taimaka mana matuƙa a matsayinmu na wuri saboda tana cikin Sahel kuma tana kusa da wuraren da barazanar ta fi ta’azzara,” in ji Ekman. Yanzu ƙalubalen zai fi wahala inji shi, domin shiga yankin sai an samu daga wajen Nijar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like