No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohon shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega ya buƙaci a gudanar da bincike kan hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke kan rikicin zaɓen gwamnan Kano.

Alfijir labarai ta rawaito cewa kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja a ranar 17 ga Nuwamba, 2023 ta soke zaɓen gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP tare da bayyana abokin hamayyarsa Nasiru Gawuna na jam’iyyar adawa ta APC a matsayin wanda yayi nasara.

KU KUMA KARANTA: NNPP ta shigar da ƙara gaban Kotun Ƙoli kan shari’ar gwamnan Kano

Amma a cikin kundin bayanan hukuncin da kotun da aka fitar kwanaki huɗu bayan yanke hukuncin, ta bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen a ƙarshen takardar.

Jaridar ta rawaito cewa fitar takardar hukuncin ta haifar da ruɗani tare da gudanar da zanga-zangar adawa da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara a Kano.

Da yake magana a gidan Talabijin na Channels TV’s ta cikin shirin Politics Today, a ranar Litinin, Farfesa Jega ya bayyana hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na Kano da ke cin karo da juna a matsayin “abin takaici ne matuƙa.”

“Babu shakka… wannan sabon lamari da ya faru game da lamarin a Kano abin takaici ne. Baya ga Chidi Odinkalu, na ji kuma na karanta yadda manyan lauyoyi da yawa a Najeriya suna ƙalubalantar abinda ya faru.”

“Za ku yi tsammanin kotuna musamman a matakin ɗaukaka ƙara zasu yi irin wannan abun? Amma abin gaskiya abin mamaki ne.” Ina ji shi

A cewarsa “Yanayin da aka bayar a matsayin rubutaccen hukuncin ya saɓa wa wanda aka karanta a cikin kotun, tabbas hakan abin mamaki ne kuma abin takaici ne matuƙa.

“Na yarda, ni ba lauya ba ne, amma na yarda cewa akwai buƙatar a yi cikakken bincike akan wannan abu.” In ji Jega

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...