No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan sanda sun ceto ɗaya daga cikin ɗalibai mata biyar da aka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma da ke jihar Katsina.

An yi nasarar ceto ɗalibar ce bayan wani samame da Rundunar ’yan sandan ta kai a ranar Litinin.

A cewar kakakin rundunar, ASP Abubakar Aliyu, an ceto ɗalibar wadda ba a bayyana sunan ta ba saboda dalilai na tsaro ne a ƙauyen Bilbis da ke Jihar Zamfara makwabciyar Jihar Katsina.

KU KUMA KARANTA: ’Yan ta’adda a Katsina sun kashe kwamandan jami’an tsaro

Ya jaddada ƙudirin rundunar na yin amfani da wadatattun kayan aiki don ceto sauran ɗaliban huɗu daga da aka yi garkuwa da su.

“Yayin da wadda aka ceto ke samun kulawar likita, Kwamishinan ’Yan sanda ya jinjina wa jami’an rundunar, ya kuma buƙaci jama’a su riƙa taimakawa da bayanai masu muhimmanci don inganta tsaro,” in ji sanarwar.

A ranar 4 ga watan Nuwamba, 2023, mahara suka sace ɗalibai mata biyar a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma, inda daga bisani ’yan sanda suka tabbatar da kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi da sace ɗaliban.

An sace ɗaliban ne a gidansu da ke bayan makarantar Mariamoh Ajiri Memorial International daura da hanyar Tsaskiya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...