No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotun ɗa’ar ma’aikata ta dakatar da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC daga shiga yajin aikin da suka shirya yi a ranar talata.

Alfijir Labarai ta rawaito Alƙalin kotun, mai shari’a Benedict Kanyip ne ya bada umarnin dakatar da yajin aikin bayan ƙarar da gwamnatin Najeriya da ministan shari’ar ƙasar suka shigar gaban kotun, don neman kotun ta hana su shiga yajin aikin, saboda hakan zai iya jefa ‘yan ƙasar cikin ƙarin wahala.

Lauyan masu gabatar da ƙarar Barista Tijani Gazali ya ce matsawar ba a dakatar da ƙungiyoyin daga shiga yajin aikin ba, za a iya samun tayar da hargitsi tare da kawu ruɗani a faɗin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya za su tsunduma yajin aiki

Yayin da yake hukuncin, alƙalin kotun ya ce, kotun na da hurumin shiga tsakani domin hana duk wani abu da ka iya tayar da hankula a ƙasar.

Mai shari’a Kanyip ya yi amfani da sahe na 17 da 19 na ƙundin dokokin kotun wajen dakatar da yajin aikin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...