No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wata kotu a Amurka ta umurci Jami’ar Jihar Chicago da ta bai wa Atiku Abubakar damar ganin takardun karatun Shugaban Najeriya Bola Tinubu.

Alƙaliyar kotun, Nancy Maldonado, ta yi watsi da buƙatar Tinubu na ƙin amincewa Atiku ya ga takardun, inda ta ba da wa’adin kwanaki biyu ga Jami’ar don miƙa wa Atiku takardun.

Ta kuma amince da hukuncin da alƙalin wata kotun majistre a Amurka, Jeffery Gilbert ya yanke a ranar 20 ga Satumba, wanda ya umarci Jami’ar ta Chicago da ta saki takardun karatun Tinubu kamar yadda Atiku ya buƙata, inda ta jaddada cewa Atiku yana da damar samun takardun.

A cewar alƙaliyar, dole ne Jami’ar ta kammala duk wani abu da ya kamata don sake takardun nan da ranar Talata.

Idan za a iya tunawa, ɗan takarar shugaban ƙasa a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakara, ya garzaya wata kotu a Amurka domin ta tilasta wa jami’ar Chicago ta saki takardun karatun Tinubu, domin hakan zai ba shi damar ƙalubalantar zaɓen shugaban ƙasa na ranar 25 ga watan Febrairu.

Ɗan takarar na PDP ya buƙaci samun takardun ne don amfani da su a kotunan Najeriya wajen tabbatar da hujjarsa cewa takardun Tinubu na jabu ne.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...