No menu items!

Sample Page Title

Date:

Muƙaddashin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya bayyana damuwa kan zanga-zangar da ƙungiyoyin ƙwadago suka shirya yi, inda ya yi gargaɗin cewa ‘yan sanda ba za su lamunci duk wani abu da zai kawo rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar ta ce ‘yan ƙasa suna da ‘yancin yin zanga-zanga kamar yadda kundin mulki ya yi tanadi amma dole ne a gudanar da ita cikin kwanciyar hankali.

Rundunar ‘yan sandan ta ce a baya irin wannan zanga-zanga tana rikiɗewa ta zama tashin hankali, saboda haka ta ke gargaɗin cewa ba za ta bari a gudanar da duk wani abu da zai kawo matsalar tsaro ba.
ACP Adejobi ya ce duk wani yunƙurin tayar da rikici a lokacin zanga-zangar ƙungiyar ƙwadago zai fuskanci fushin hukuma.

Ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya sun shirya fara zanga-zanga a faɗin ƙasar daga ranar Laraba 2 ga watan Agusta domin nuna rashin amincewa da soke tallafin mai da gwamnati ta yi.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...