No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya ayyana ranar Laraba 19 ga watan Yuli 2023 a matsayin ranar ɗaya ga watan Muharram na sabuwar shekarar 1445H.

Sultan, Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya, tun farko ya buƙaci Musulmi da su sanya ido kan ganin jinjirin watan Muharram a ranar Litinin, 17 ga Yuli, 2023.

Al-Muharram shi ne watan farko a kalandar Musulunci kuma ana ganin wata ne mai alfarma.

An umurci musulmi da su gudanar da azumin a ranakun 9 da 10 ga wata, wanda ake ƙira Tasu’a da Ashura.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Ita ma wannan ranar tana da mahimmaci domin ta kasance ranar da Allah ya ceci Annabi Musa daga hannun Fir’auna na Masar, inda ya ƙetare Teku tare da mutanensa.

Majalisar Sarkin Musulmi ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Talata, 18 ga Yuli, 2023.

“Saboda rashin samun ingantaccen rahoton ganin jinjirin watan a Najeriya, an ayyana ranar Laraba 19 ga watan Yuli 2023 a matsayin ranar farko ta MUHARRAM 1445H,” in ji sanarwar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...