No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hedikwatar tsaro ta ce dakarun ‘Operation Forest Sanity’ tare da haɗin gwiwar hedkwatar tsaro na musamman sun kashe ‘yan ta’adda shida tare da ƙwato makamai da alburusai a jihar Kaduna.

Daraktan ayyukan yaɗa labarai na tsaro Musa Ɗanmadami ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Manjo Janar Ɗanmadami, ya ce a ranar Juma’ar da ta gabata ne sojojin suka gudanar da wani samame a ɓoye a yankunan ‘yan ta’adda a ƙauyen Maidaro da ke ƙaramar hukumar Giwa tare da tuntuɓar ‘yan ta’addan.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama 161

Ya ce an kawar da ‘yan ta’addan shida a yaƙin wuta da ya ɓarke. A cewarsa, an ƙwato bindigogin AK 47 guda biyar, alburusai mai tsayin 7.62 x 39 na musamman guda 192, alburusai 74 na musamman masu tsayin 7.62 x 54 da kuma na AK 47 guda tara.

“An ƙwato IED guda uku, rediyon Baofeng guda uku, PKM ɗaya, babura uku da sauran kayayyaki iri-iri.

“Babban kwamandan sojojin ya yaba wa sojoji tare da ƙarfafa gwiwar jama’a da su baiwa sojojin da sahihan bayanai masu inganci kan ‘yan ta’adda da duk wasu ayyukan aikata laifuka a yankinsu,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...