No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu mata biyu shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce an yi garkuwa da mutanen ne a hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari yayin da suke komawa gida bayan halartar bikin rantsar da Gwamna Uba Sani a ranar Litinin.

Shugaban ƙungiyar ci gaban masarautar Birnin Gwari, BEPU, Ishaq Usman, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba cewa lamarin ya faru ne a unguwar Manini da ke kan hanyar.

KU KUMA KARANTA: Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani limamin cocin Katolika a Imo

A cewarsa, ‘yan bindigar sun tare hanya tare da yin garkuwa da waɗanda aka kashe tare da wasu matafiya a ranar Talata.

Matan ‘yan siyasar sun haɗa da shugabar mata ta APC a Birnin Gwari, Lami Awarware, da mataimakiyarta Haulatu Aliyu.

Har yanzu dai masu garkuwa da mutanen ba su tuntuɓi iyalan waɗanda aka sace ba.

Har ila yau gwamnatin jihar da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, (PPRO), Mohammed Jalige, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayani kan lamarin ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...