No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dogayen layukan mai sun dawo a gidajen sayar da mai a faɗin biranen Najeriya tun bayan da sabon shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man.

A jiya Litinin ne Tinubun ya sanar da cire tallafin a jawabinsa na farko bayan rantsuwar kama aiki inda ya ce kasafin ba ya cikin kasafin kuɗin da ya gada daga gwamnatin Buhari.

Wasu rahotanni na cewa a birane irin su Lagos da Abuja ana sayar da man a wasu wuraren a kan kusan naira 600 a kan lita ɗaya ƙari daga 185 a kan lita a yau Litinin. Kamar a birnin Damaturu 350 ne litar mai a wasu gidajen man. Sannan ga dogayen layuka, saboda wasu gidajen man sun ƙi buɗewa.

KU KUMA KARANTA: Sabon Gwamnan Kano Abba Gida-Gida, ya naɗa shugaban ma’aikata da sakataren gwamnati

Sai dai kuma kamfanin mai na ƙasar NNPC ya sanar cewa akwai wadataccen mai a ƙasar saboda haka babu dalilin da zai sa mutane su shiga fargabar sayen man.

‘Yan ƙasar da dama na kokawa kan yadda suke shafe tsawon lokaci a kan layi domin sayen man.

Tinubu ya ce za a yi amfani da kuɗin tallafi wanda ya ce a yanzu wasu attajirai ne kawai suke cin moriyarsa, wajen bunƙasa wasu fannonin da jama’a za su fi amfana.

Ba a san ko tun daga jawabin nasa gwamnati ta dakatar da tallafin ba kenan.

Masana harkokin tattalin arziƙi na nuna cewa tasirin cire tallafin zai haddasa tsadar sufuri da kayayyaki.

4 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...