No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa ta gargaɗi ‘yan Najeriya game da sanarwar ‘damfara’ da wasu marasa gaskiya suka yi ta hannun hukumar EFCC na ƙarya.

Faɗakarwar zamba na iya kasancewa ta hanyar ƙiraye-ƙirayen ƙarya da aka ce ta fito ne daga teburin taimakon hukumar.

Kakakin ta, Wilson Uwujaren, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Talata, inda ya ce ‘saƙon damfara’ da ake ta yaɗawa a shafukan sada zumunta na bogi ne.

KU KUMA KARANTA: Buhari ya ƙaddamar da hedikwatar hukumar kwastam, ya lanƙwame sama da biliyan 19

“Don kaucewa shakku, EFCC ba ta da irin wannan tebur, kuma duk wani bayani da ake zaton ya fito daga hukumar EFCC HELP DESK ba ta samo asali daga EFCC ba.

“Yin amfani da EFCC da mawallafin saƙon damfara ya yi na mugun nufi. “Yana da muhimmanci a sanar da jama’a, domin hukumar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba idan har wani ya zama wanda aka zalunta a fili ta hanyar zamba.

“Don haka hukumar ta shawarci jama’a da su yi taka-tsan-tsan tare da tantance duk wani bayani da ke da alaƙa da su,” inji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

4 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...