No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani magidanci mai shekaru 34, Segun Bashiri, a ranar Alhamis, ya gurfana a gaban wata kotun majistiri ta Okitipupa dake jihar Ondo bisa zargin satar buhu 50 na simintin Ɗangote wanda kuɗinsa ya kai N235,000.

Wanda ake ƙarar, wanda ba a bayar da adireshinsa ba, yana fuskantar tuhuma biyu, wanda ya shafi aikata laifuka da sata.

Ɗan sanda mai shigar da ƙara, ASP Zedekiah Orogbemi, ya shaida wa kotun cewa wanda ake ƙara da ɗaya wanda har yanzu ba a garƙame shi ba a ranar 12 ga watan Janairu da misalin ƙarfe 12:30 na safe a wani gini da ke kan titin Okitipuoa-Ikoya a cikin Okitipupa, sun haɗa baki wajen aikata laifi da kuma sata.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun ceto mutane 5, sun kama 17 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a Nasarawa

Mista Orogbemi ya ce wanda ake ƙara da sauran manyan ma’aikata ne a wani gini, mallakin wani Mathew Kawonise, sun sace buhunan siminti da aka yi niyyar yin aiki dasu.

A cewar sa, laifukan ana hukunta su ne a ƙarƙashin sashe na 412 da 390(9) na kundin laifuka, Cap. 37, Vol. 1, Dokokin Jihar Ondo, 2006. Sai dai wanda ake tuhumar ya ƙi amsa laifin da ake tuhumarsa da shi. Alƙalin kotun, Mista Chris Ojuola, ya bayar da belin wanda ake ƙara a kan kuɗi N100,000, tare da mutane biyu da za su tsaya masa.

Ojuola ya ce dole ne waɗanda za su tsaya masa su kasance a ƙarƙashin ikon kotun kuma su gabatar da shaidun biyan haraji na shekaru biyu da aka yi wa gwamnatin jihar.

Daga nan ya ɗage ci gaba da sauraren ƙarar har zuwa ranar 6 ga watan Mayu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

6 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...