No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohon jami’in rundunar kwastam, ACG Kamilu Ado ya rasu ana saura kwanaki shida zaɓe a Kano, sai ɗan takarar shugaban Ƙasa na jam’iyyar NNPP, Dokat Rabiu Musa Kwankwaso ya ce a bawa ɗan Marigayin takarar bayan mahaifinsa ya rasu, cikin ikon Allah sai ya lashe zaɓen Ɗan Majalisar Tarayya Mai wakiltar ƙananan hukumomin Wudil da Garko.

Abubuwan da ya kamata ku sani game da ɗan da ya gaji takarar mahaifinsa, Sheikh Abdul Hakeem Kamilu Ado

Sunan sa Shekh Abdulhakeem Kamilu Ado Wudil, yana da Shekaru 30,Bayan Mutuwar Mahaifinsa kwana shida ga zaɓe jam’iyyar NNPP ta bashi takarar saboda nagartarsa.

KU KUMA KARANTA: Yadda yaro ɗan shekara 20 ya sace mahaifiyarsa, ya karɓi kuɗin fansa naira miliyan 30 a Zamfara

Ya kasance mahaddacin Alqur’ani
Makarancin hadith da Fiqh.

Yayi karatun digirinsa na farko a jami’ar ABU Zaria, kuma yanzu haka yana karatun digirinsa na biyu a jami’ar.

Malamin jami’a ne a jami’ar Al-Istiqama da ke Sumaila a Kano.

Yana da cibiyar koyarwa wato Markaz ta koyarwar addini a masallacin jami’ar KUST da ke Wudil da kuma sauran majalisai.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...