No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Shafaatu Dauda,kano

Hukumar zaɓe ta ƙasa reshan jihar Kano ta bayyana cewa wasu matasa sun farwa ma’aikatan ta a yankin ƙaramar hukumar Rimingado har suka ƙwace katinan zabe guda 158.

Kakakin hukumar a Kano Ahmad Adam Maulud ne yabbaya hakan.
ya ce ‘’ yanzu haka matasan suna hannun jami’an yan sandan jahar Kano domin gudanar da bincike akan lamarin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan siyasa na sayen katin zaɓe -INEC

Matasan da ake zargi sun hada Abduljafur mai shekaru 22 da kuma Saifullahi Rabo mai shekaru 23, da ake zargin yaran wani tsohon dan majalissar dokokin jahar Kano ne.

Wakiliyarmu tayi ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, amma lamarin ya ci tura .

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...