No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Najeriya ta amince ta ƙulla yarjejeniya da wani kamfani a Koriya ta Kudu da zimmar gyara matatar man fetur ta Kaduna da ke arewacin ƙasar.

Shugaban kamfanin mai na Najeriya NNPC, Mele Kyari, shi ne ya saka hannu a madadin Najeriya yayin taro kan harkokin lafiya da tawagar ƙasar ke halarta a Koriya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari.

Sanarwar da NNPC ya wallafa a shafinsa na Twitter ta ce nan gaba kaɗan za a fara zagayen duba gyaran da za a yi.

A ƙarshen shekarar 2021 ne gwamnatin Najeriya ta ware fiye da dala biliyan ɗaya don gyara matatar mai ta da ke birnin Fatakwal, aikin da ta ce ana ci gaba da yi.

Kazalika, za a ci gaba da irin wannan aiki a matatar ta garin Warri na Jihar Delta.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...