Bukin Sallah: El-Zakzaky Ya Raba Buhunan Hatsi, Da Tsabar Kudi Ga ’Yan Jarida Na Kaduna

0
332

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

YAYIN da ake Kokarin gudanar da bukukuwan Sallah, Shugaban Kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN), da aka fi sani da Shi’a, Sheikh Ibraheem Yakubu El-Zazzaky ya raba buhunan hatsi da suka hada da shinkafa, tare da kudi ga magoya bayansa dake Kaduna don samun isasshen abinci bikin sallah.

Idan dai za a iya tunawa dai, a baya an raba daruruwan buhunan hatsi ga matan Kiristoci zawarawa da marayu a kudancin Kaduna a lokacin da aka fara Azumin watan Ramadan.

Kayayyakin da suka fito ta hannun Fasto Yohanna Buru mai kula da Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Church Kaduna na daga cikin rabon kayan abinci da El-Zakzaky ya yi na Sallah ga Musulmai da Kirista a fadin kasar nan.

Fasto Buru, ya ce dalilin da ya sa El-Zakzaky ya raba kayan abincin shi ne karfafa alaka tsakanin Musulmi da Kirista a kasar nan.

Buru ya kara da cewa a shekarun baya, Sheikh El-Zakzaky yana rabon kayan abinci a lokutan bukukuwan Ramadan da na Sallah ga miliyoyin ‘yan Najeriya na gida da waje ko da yana tsare a Abuja da kuma gidan yarin kaduna.

Yayin da yake wayar da kan al’ummar musulmi a fadin duniya gaba daya, ya yi kira ga al’ummar musulmi da su dauki darasi a tsawon kwanaki 30 na watan Azumin Ramadana da inganta fahimtar juna da fahimtar juna a tsakanin kungiyoyi daban-daban na kasar nan.

Ya koka da rashin tsaro da ya dabaibaye kasar nan inda ya ce akwai bukatar gwamnati ta kara kaimi wajen tabbatar da tsaron ‘yan Najeriya.

A azurfa daya daga cikin wakilan Aliyu Mohammad wanda shi ne wakilin gidan rediyon kasar Iran ya bayyana farin cikinsa a madadin Ramadan ya godewa jagoran Harkar Musulunci da ya tuna da su a cikin watan Ramadan da kuma lokacin bukukuwa.

Ya yi kira ga limaman Musulmi da su ci gaba da yi wa kasa addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here