Allah Ya Yi Wa Sheikh Ahmad Bamb Rasuwa

0
389

Daga Rabo Haladu Da Imrana Mustapha

Allah Ya yi wa babban malamin addinin nan na Kano Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, wanda aka fi sani da Kala Haddasana rasuwa a yau Juma’a.

Wasu iyalansa ne suka tabbatar wa da manema labarin rasuwar.

Fitaccen malamin ya yi fice ne a wajen karatuttukan Hadisi, inda a da can yake karantarwar a Masallacin BUK amma daga baya ya bude nasa wajen mai suna Darul Hadis.

Malamin ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya inda ya kwana ɗaya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.I

Iyalansun sanar da cewa anyi jana’izar malamin a Masallacin Darul Hadis da ke unguwar Tudun Yola a birnin Kano bayan Sallar Juma’a.

Wani daga cikin ƴaƴansa Abdul ya shaida cewa ya kusan shekara 82, don an haife shi ne a shekarar 1940.

Kala Haddasana kamar yadda aka fi saninsa da shi ɗan asalin ƙasar Ghana ne kuma a can aka haife shi.

“Ya dawo Najeriya ne bayan da ya yi karatun digirinsa a Saudiyya, sai ya koma Najeriya ya fara koyarwa a Jami’ar Bayero ta Kano har ya yi digirin-digirgir.

“Ya koyar a fannin Islamic Studies kuma ya jima yana koyarwar,” a cewar ɗan nasa.

Malamin ya bar yara 28 zuwa 30 kamar yadda ɗan ya shaida mana


Leave a Reply