No menu items!

Sample Page Title

Date:

Iyayen wata ɗalibar aji huɗu aa Jami’ar Abuja, Murjanatu Zubairu, da ta ɓace ranar Juma’a, sun ce ta mutu. 

Kawun marigayiyar, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti ne ya tabbatar wa wakilin mu da rasuwarta a ranar Litinin.

Ya ce iyayen Murjanatu sun  sanar da shi cewa bayan gudanar da bincike mai zurfi sun gano cewa ta rasu ne a wani mummunan hatsarin mota a yammacin ranar Juma’a a kan hanyar Lugbe.

A cewarsa, iyayen yarinyar sun gano gawarta ne a dakin ajiye gawarwaki na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja da ke Gwagwalada lokacin da suka je asibitin domin tambayar ko an kawo ta ba lafiya ko wani abu makamancin haka.

KU KUMA KARANTA: Mutum 3 sun rasu, an jikkata 10 a rikicin sojoji da ’yan Keke NAPEP a Yobe

Alhaji Zubairu ya ce, “iyayenta sun ƙira ni sun sanar da ni cewa ta rasu ne a hatsarin mota da ya rutsa da ita a babban titin Lugbe zuwa filin jirgin Abuja.”

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) na shiyyar Lugbe, Sunday Ajokotola, ya tabbatar da cewa mutane 10 ne hatsarin mota ya rutsa da su, inda mace ɗaya da maza uku suka ƙone ƙurmus a ranar Juma’ar da ta gabata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...