No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kungiyar ɗalibai ta ƙasa a Sudan, ta yi ƙira ga hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, (NIDCOM), da ta yi ƙoƙarin kwashe su daga Sudan.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Gabriel Odu, sashin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na NIDCOM, ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Mista Odu ya ce kiran na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da ɗaliban suka aikewa hukumar. Ya ce hukumar ta samu takardar neman korar mutanen musamman waɗanda ke birnin Khartoum, babban birnin ƙasar Sudan.

KU KUMA KARANTA: Yadda mutumin da ya yi tattaki daga Najeriya zuwa Saudiyya a kan keke yayi karanbatta da ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga

Tun da farko, Abike Dabiri-Erewa, shugabar NIDCOM, ta bayyana damuwarta kan halin da ɗaliban Najeriya ke ciki a Sudan.

Misis Dabiri-Erewa ta ce tashin hankalin da ake yi tsakanin sojojin Sudan da ƙungiyar Rapid Support Forces, RSF, na da matuƙar damuwa.

Hukumar ta ba da tabbacin cewa hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA mai kula da kai ɗaukin gaggawa na tuntuɓar tawagar Najeriya dake Sudan da sauran hukumomin da abin ya shafa.

Misis Dabiri-Erewa ta buƙaci ɗaukacin ɗaliban Najeriya da ke Sudan da kuma ‘yan Najeriya mazauna Sudan, da su kasance masu lura da tsaro kuma su natsu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...