No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar lokitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shiga bayan kwana 17, inda likitocin za su ci gaba da aiki daga yau Asabar.

Shugaban ƙungiyar National Association of Resident Doctors (NARD), Dakta Emeka Orji, ya faɗa wa BBC cewa sun jingine yajin ne bayan gwamnatin tarayya ta amince da kafa gidauniyar horaswa ta ‘Medical Residency Training Fund’.

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta fara shirin biyan su alawus na rage wahalar aikin da suke sha a asibitocin gwamnati sakamakon ficewar likitoci zuwa ƙasashen waje, kamar yadda suka nema.

A cewar Dakta Orji, waɗannan ne manya daga cikin buƙatun nasu kuma za su zauna don duba cigaban da aka samu nan da mako biyu.

KU KUMA KARANTA: Likitocin Najeriya sun yi barazanar yajin aiki a Nasarawa

Likitocin waɗanda su ne kashi 60 cikin 100 na kafatanin likitocin gwamnati a Najeriya, sun ƙaurace wa ayyuka ranar 26 ga watan Yuli, suna masu neman ƙarin kulawa da kuma inganta yanayin aikin nasu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...