Ɗaruruwan mutane sun fito zanga-zanga a birnin tarayya Abuja (Hotuna)

0
41
Ɗaruruwan mutane sun fito zanga-zanga a birnin tarayya Abuja (Bidiyo)

Ɗaruruwan mutane sun fito zanga-zanga a birnin tarayya Abuja (Hotuna)

A ranar Alhamis, 1 ga watan Agusta, 2024 masu zanga-zanga sun fito ƙwansu da ƙwarƙwatansu, domin nuna fushin su da damuwa akan talauci da rashin tsaron da yake damunsu.

A babban birnin tarayya Abuja, mata da dama sun fito har da tsofaffi domin yin wannan zanga-zangar.

“An kashe mana mazaje, an barmu da marayu, ga yunwa, ina fama da rashin lafiya amma na fito dan yin wannan zanga-zangar lumana” in ji wata mata.

KU KUMA KARANTA: An tarwatsa masu zanga-zanga kan ƙoƙarin kunna wuta a ƙofar gidan gwamnatin Kano

Wakilin Neptune Hausa, Abubakar Kado, ya ɗauko mana rahoton cewa ana jefa borkonon tsohuwa, wato “tear gas” a yayin zanga-zangar.

‘Yan zanga-zangar na cewa su koma baya saboda kar borkonon tsohuwar ta same su.

Kalli hotunan Zanga-zangar a nan:

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here