No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da ba a san adadinsu ba da ke tafiya a kan hanyar East-West a Ugheli, jihar Delta da ke kudu maso-kudancin Najeriya.

Direban motar ya ranta a na kare ba tare da samun ko rauni ba. Kakakin Rundunar ƴan sandan Jihar Delta Edafe Bright ya bayyana cewa wataƙila fasinjojin cikin motar ɗalibai ne da ke dawowa daga makarantarsu a Calabar, Jihar Cross River ranar Juma’a da daddare, kafin a yi garkuwar da su a ƙaramar motar bas da suke ciki.

Ya ce ya zuwa yanzu ba a buƙaci a biya kuɗin fansa ba. Sai dai kuma, ƴan sanda sun bazama neman mutanen da suka yi garkuwa da ɗaliban.

“Hedkwatar ƴan sanda na sane da wannan mummunan al’amari, kuma muna yin duk mai yiwuwa don tabbatar da an kuɓutar da su ba tare da wata matsala ba,” in ji Bright a saƙon da ya wallafa a shafin X.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindigar da suka sace ɗalibai 286 sun buƙaci kuɗin fansa naira biliyan ɗaya

Lamarin ya faru ne kwanaki kaɗan bayan ƴan bindiga sun sace ɗaliban jami’a da dama a jihar Cross River mai maƙwabtaka.

A Najeriya, ƴan bindiga na yawan garkuwa da ɗalibai a makarantunsu tare da neman kuɗaɗen fansa kafin su sako su, lamarin da ke ƙara ta’azzara sha’anin tsaro a ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...