No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyoyin mata sun nemi a ba su damar samun kujeru masu yawa a majalisun ƙasa da na jihohi

Daga Shafaatu Dauda Kano

Gamayyar ƙungiyoyin mata ta ƙasa waɗanda suka haɗa da FIDA, WRAPA, da WACOL, sun gabatar da daftarin dokar da ke neman ƙarin kujeru na musamman ga mata a Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai, da kuma majalisun dokokin jihohi.

Daftarin, wanda aka gabatar wa kwamitin sake nazari akan kundin tsarin mulki na Majalisar Dattawa a Kano, na neman a ware kujeru 37 ga mata a majalisar dattawa, guda ɗaya daga kowace jiha da Abuja.

KU KUMA KARANTA: A kawo ƙarshen cin zarafin mata da nuna ƙyama ga ‘yan mata a jihar Nasarawa, daga Fa’izatu Aliyu Doma

Haka kuma, suna neman kujeru 47 a majalisar wakilai da kuma kujeru 3 ga mata a kowace majalisar jiha.

A cewar Dr. Mohamed Mustapha Yahya, wannan yunkuri yana da nufin magance ƙarancin wakilcin mata a siyasa, duba da cewa su ke da kashi 45 zuwa 49 cikin ɗari na masu kada ƙuri’a a lokacin zaɓe.

Habiba Ahmed daga kungiyar WRAPA ta buƙaci gwamnati da ta amince da hakan tare da gyara tsarin zaɓe domin inganta wakilcin mata a harkokin shugabanci.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...