No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar Manchester United ta sallami kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United, ta sallami kocinta, Erik ten Hag daga aiki.

Ƙungiyar ta fitar da sanarwa ne a ranar Litinin, inda ta ce matakin zai fara aiki nan take ne.

Wannan dai ya biyo bayan rashin nasara da ƙungiyar ta yi a hannun West Ham United da ci 2 da 1 a ranar Lahadi.

“Erik ten Hag ya rabu da matsayinsa a matsayin mai horas da ’yan wasan Manchester United. Mun gode masa da irin gudunmawar da ya ba mu tsawon lokacin da ya kasance tare da mu sannan muna masa fatan alheri.

“Ruud van Nistelrooy zai riƙe ƙungiyar a matsayin kocin wucin gadi kafin a nemo sabon mai horaswa.”

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Jigawa ya kori Kwamishina kan zargin lalata da matar aure

Rashin ƙoƙarin da ƙungiyar ke yi a kakar wasa ta bana, ya kai ga rasa aikin ten Hag.

Kocin wanda ɗan asalin ƙasar Netherlands ne, ya samu nasarar lashe kofin FA a kakar wasa ta bara.

Ten Hag ya shafe tsawon shekara biyu da rabi a ƙungiyar kafin sallamarsa a ranar Litinin.

Yanzu haka Manchester United na mataki na 14 a teburin gasar Firimiyar Ingila, bayan buga wasanni bakwai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...