No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kungiyar kafafen yaɗa labarai ta yanar gizo Association of Online Media Guild, ta taya gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano murnar samun nasara a kotun ƙoli.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta raba wa manema labarai ta hannun shugabanta na riko, Abdullateef Abubakar Jos.

A ranar Juma’a nan ne dai kotun ƙoli ta tabbatar da Abba Kabir Yusuf a matsayin Gwamnan Jihar Kano bayan da kotun sauraren ƙararrakin zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara suka soke nasarar sa.

KU KUMA KARANTA: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Dauda Lawan a natsayin gwamnan jihar Zamfara

Ƙungiyar ta buƙaci gwamnan jihar da ya kiyaye kyakkyawar alaƙar da yake da ita da ’yan jarida na yanar gizo, domin Kano ce ta biyu da ta ke da ɗimbin masu kafafen yaɗa labarai na yanar gizo baya ga jihar Legas.

A ƙarshe ƙungiyar ta buƙaci Gwamnan da ya ƙara inganta ayyukan more rayuwa domin cigaban jihar Kano.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...