No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumomin Masar sun kama wani ɗan jarida da ya wallafa labarin yana zargin jami’ai da hannu wajen safarar kuɗi da makamai da zinare zuwa ƙasar Zambiya.

Zargin da Karim Asaad ya yi ya biyo bayan kama wani jirgin hayar da jami’an Zambiya suka yi a filin jirgin saman Lusaka.

An ce yana ɗauke da kuɗi sama da dala miliyan 5 (£3.9m) da kuma bindigu, alburusai da fiye da kilogiram 100 na zinare. Takardun waɗanda ake zargin sun fito ne daga wani bincike na Zambiya an zargi wasu sojoji da ‘yan sandan Masar da dama a matsayin waɗanda ake tuhuma.

Ƙungiyar ‘yan jaridu ta ƙasar Masar ta ce Mista Asaad shi ne ɗan jarida na 24 da ake tsare da shi a ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar ‘yan jarida a Yobe sun gana da shugaban majalisar jihar

Mista Asaad yana aiki ne da shafin labarai na Matsda2sh.

Abokan aikin Mista Asaad sun zargi jami’an tsaro da cin zarafin matarsa ​​da yaronsa a lokacin da aka kama shi a ranar Asabar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...