No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙasar Amurka za ta hana wasu ‘yan Ghana bizar shiga ƙasarta

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka a ranar Litinin ta sanar da cewa, Amurka za ta taƙaita ba da bizar shiga ƙasar ga mutanen da Washington ke gani a matsayin barazana ga fannin dimokuraɗiyya a Ghana.

Matakin na zuwa ne gabanin zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokoki da za a yi a ƙasar da ke yammacin Afirka a ranar 7 ga watan Disamba.

”Yunƙurin taƙaita ba da bizar zai shafi wasu ‘yan Ghana waɗanda ke yin katsalandan a fannin dimokuraɗiyya ba wai ga ‘yan ƙasa baki ɗaya ko kuma gwamnatin Ghana ba”, a cewar wata sanar da Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya fitar.

A baya dai Ghana ta sha gudanar da zaɓukanta cikin lumana da sahihanci, sai dai a bana ana ci gaba da samun fargaba da kuma yiwuwar koma-baya ta fuskar dimokuraɗiyya a ƙasar sakamakon zarge-zargen rashin bin ƙa’idoji gabanin zaɓen da ke tafe.

KU KUMA KARANTA: Amurka ta zargi China Da yin harshen Damo a Yaƙin da Rasha ke yi a Ukraine

Zaɓen na watan Disamba zai kasance babban zaɓe karo na tara a jere tun bayan komawar ƙasar tsarin dimokuraɗiyya a shekarar 1992.

A watan da ya gabata ne babbar jam’iyyar adawa ta Ghana, National Democratic Congress (NDC), ta gudanar da zanga-zangar neman a tantance sunayen masu kaɗa ƙuri’a a faɗin ƙasar.

Ta yi zargin cewa ta gano dubban mutane waɗanda ba su cancanci yin zaɓe ba sannan kuma an cire sunayen wasu masu kaɗa ƙuri’a daga rajistar zaɓe.

Shugaban ƙasar Nana Addo Dankwa Akufo-Addo zai sauka daga mulki a bana bayan wa’adinsa na biyu kuma na ƙarshe na shekaru huɗu.

‘Yan takara 13 ne hukumar zaɓe ta amince da su tsaya takarar zaɓen shugaban ƙasa a Ghana.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...