No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya buƙaci sojojin Najeriya da su kafa sansanin soji a dajin Sambisa domin daƙile ayyukan masu tayar da ƙayar baya yadda ya kamata.

Zulum ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da mambobin Kwamitin Majalisar Wakilai kan harkokin soji suka kai masa ranar Laraba a Maiduguri, babban birnin jihar.

Gwamnan ya kuma buƙaci sojojin da su kafa sansanin soji a gaɓar Tafkin Chadi da kuma tsaunin Mandara wanda ke zama mafakar ‘yan ta’adda.

“Akan batun kawo ƙarshen ta’addancin gaba ɗaya, akwai buƙatar gwamnati ta kafa sansanin soji a Sambisa, gaɓar Tafkin Chadi da tsaunin Mandara.”

Ya buƙaci Majalisar Dokoki ta ƙasa da ta tabbatar da isassun kason makamai don magance matsalar tsaro.

KU KUMA KARANTA: Abin da ya sa ba a cika satar ɗalibai ba a Borno — Zulum

Zulum ya kuma bayyana buƙatar tabbatar da tsaro a Jihar Borno wadda ta yi iyaka da ƙasashe uku, musamman ta fuskar daƙile kwararowar ƙananan makamai da ke ƙara rura wutar matsalar tsaro a Arewacin ƙasar.

Ya ƙara jaddada ƙudurinsa na tallafa wa sojoji a fagen yaƙi da ta’addanci, yana mai cewa kawo yanzu tubabbun ‘yan Boko Haram 190,000 ne suka miƙa wuya ga mahukunta.

A cewar Zulum, kula da ɗimbin tubabbun ‘yan Boko Haram wani ƙalubale ne da ke buƙatar goyon bayan masu ruwa da tsaki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...