Connect with us

Labarai

Zawaciki: Unguwar da saurayi ke neman budurwa a ranar sallah a Kano

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hausawa suka ce ba a neman budurwa ranar sallah, saboda kowace budurwa har da ƙazama, tana caɓa ado, ta yi kwalliyar sallah. To amma a unguwar Zawaciki da ke birnin Kano ba haka abin yake ba. Domin kuwa akwai wani wuri mai tarihi da ɗaruruwan al’umma ke taruwa, sau biyu a shekara domin bukukuwan sallah. Wato sallah ƙarama da sallah babba. Kuma kowace sallah, rana ɗaya ake zuwa. Ana ƙiran wajen da Masallacin Zawaciki Idin Kwakwa.

Duk saurayin da yake so ya samu budurwa, to nan zai je, haka ma budurwar da take so ta samu saurayi to nan za ta je. Idan kuma kana da budurwa to da ita za ka je wajen. Akwai ƙauyuka da suke Kano da suke halartar wannan wuri, irinsu Gwarzo, Garun Malam, Kura da Madobi. Sannan akwai ‘yan ƙwaryar cikin birnin Kano da suke zuwa wannan waje na masallacin Zawaciki Idin Kwakwa, dake unguwar Zawaciki.

Babban abin da ake so a wannan waje shi ne saurayi ya sayawa budurwarsa Kwakwa. Wurin cika yake ya batse da jama’a hululu, samari da ‘yan mata da yara ƙanana da sauran masu son shaƙatawa sune suke cika wurin. Ana fara taro a wannan waje da zarar an idar da sallar Idi. Ana tanɗe-tanɗe da lashe-lashe a wannan waje. Sannan ƙarfe 5:00 na yamma ake korar kowa a wajen. Ana cashewa sosai a wajen, ana kaɗe-kaɗe da raye-raye sosai.

KU KUMA KARANTA: Yadda mahauci ya kashe matarsa saboda wayar hannu a Adamawa

Idan ka je wajen, za ka ga ‘yan mata ne da samari suke ta yawon kai-komo a wajen. Kowa za ka ganshi cikin farin ciki da annashuwa a wajen, musamman samari da ‘yan mata. Idan ka ga budurwar da kake so, to za ka mata magana ne. Haka ma budurwar idan ta ga saurayin da take so, to za ta yi ta nuna masa alamar tana sonsa, har sai ya gane.

To daman al’adar wajen shi ne idan ka cewa budurwa kana sonta, to dole ne ka je ka saya mata Kwakwa. Duk budurwar da ke wannan waje, babban abin da za ka burge ta da shi, shi ne ka saya mata Kwakwa. Tsire, balangu ko Yogot bai kai Kwakwa daraja ba a budurwa a wannan wajen. Duk budurwar da aka saya mata Kwakwa a wannan wajen, jin kanta take kamar ta fi kowa sa’a a duniya.

Wajen yana cika sosai, har ‘yan Kurna, Gwale, Rijiyar Lemo, Ɗorayi, Sharaɗa, Dala, Fagge da Nassarawa duk suna zuwa wajen. Sannan idan kana da budurwa za ka iya zuwa da ita wajen. Kuna zuwa kuma za ka je ka saya mata Kwakwa. Akwai waɗanda suke zuwa da iyalansu, sai su taho da taburma su shimfiɗa su zauna suna ta kallon yadda ake ta kai-komo a wannan waje. Su ma su ci, su sha su yi hani’an.

Masallacin Zawaciki Idin Kwakwa, yana nan a birnin Kano, hanyar Panshekara. An yi na ƙaramar sallah, saura na babbar sallah a nan gaba kaɗan. Duk mai so ya ganewa idonsa, to sai ya halarci na babbar sallah ɗin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like