Connect with us

Ƙasashen Waje

Zanga-zanga ta ɓarke a Senegal bayan sanar da ɗage zaɓe

Published

on

Jami’an tsaron Senegal sun tarwatsa dandazon jama’a da suka taru a Dakar babban birnin ƙasar ranar Lahadi domin nuna adawa da ɗage zaɓen shugaban ƙasar da aka yi, wanda a da za a yi shi ne a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaba Macky Sall ya sanar a ranar Asabar da ta gabata cewa za a jinkirta kaɗa ƙuri’ar zuwa ranar da ba a bayyana ba saboda taƙaddama kan jerin sunayen ƴan takara – matakin da jam’iyyun adawa suka yi watsi da shi.

Kimanin masu zanga-zanga 200 ne suka hana zirga-zirgar ababen hawa a babban titin birnin Dakar tare da saka shingayen na ƙonannun tayoyi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

An kama tsohuwar Firaiministar Senegal Aminata Toure, wadda a yanzu ita ce babbar ‘yar gaba-gaba a zanga-zangar nuna adawa da ɗage zaɓen shugaban ƙasa, kamar yadda ɗan majalisar jam’iyyar adawa Guy Marius Sagna ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP.

“Na tabbatar da cewa ‘yan Jandarma sun kama Aminata Toure,” in ji shi. Shugaban ƙasar Macky Sall ne ya naɗa Toure firaiminista amma daga baya ta koma jam’iyyar adawa.

Ƴan zanga-zangar

Ɗaruruwan magoya baya na adawa da ke zanga-zangar sun koma kan gefen titunan bayan ‘yan sandan kwantar da tarzoma sun harba hayaƙi mai sa hawaye. Har yanzu dai hukumomin ƙasar ba su ce komai ba kan sabon lamarin.

KU KUMA KARANTA: ECOWAS ta damu kan ɗaga zaɓen shugaban ƙasa a Senegal

Senegal dai ba ta taɓa jinkirta zaɓen shugaban ƙasa ba kuma akwai rashin tabbas kan abin da zai biyo baya.

A bara, ƙasar ta fuskanci mummunar zanga-zanga bayan da aka ɗaure jagoran ƴan adawa Ousmane Sonko, inda magoya bayansa suka ce wata dabara ce ta hana shi tsayawa takara a zaɓen.

Shekaru da dama ana kallon Senegal a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen Yammacin Afirka mafi kwanciyar hankali a tsarin dimokuraɗiyya, amma rashin ci-gaban siyasa a ƙasar ya haifar da damuwa.

Bayan sanarwar da Sall ya yi ta kafar talabijin, ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS ta nuna damuwa game da yanayin da ya kai ga ɗage zaben, tare da yin kira da a sanya sabuwar ranar zaɓe cikin gaggawa. An kuma buƙaci a kwantar da hankula da bin matakin sasantawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like