Zanga-Zanga: DSS ta musanta kai samame ofishin NLC

0
74
Zanga-Zanga: DSS ta musanta kai samame ofishin NLC

Zanga-Zanga: DSS ta musanta kai samame ofishin NLC

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta musanta kai samame ofishin ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya (NLC) da ke Abuja a daren ranar Laraba.

Neptune Prime Hausa ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun kai samame hedikwatar NLC.

A cewar ƙungiyar, jami’an tsaron sun kai samamen ne da misalin karfe 8:30 na daren Laraba.

Shugaban sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na NLC, Benson Upah, ya ce, “Sun kutsa kai ne suka yi awon gaba da wasu litattafai a hawa na 2 sannan suka kwashe tarin wasu takardu.

KU KUMA KARANTA: Jami’an tsaro sun far wa hedikwatar NLC a Abuja

“Jami’an sun yi iƙirarin cewa suna neman kayan da aka yi amfani da su a zanga-zangar #EndBadGoveranance.”

Sai dai mai magana da yawun hukumar DSS, Dokta Peter Afunanya, yayin da yake mayar da martani, ya ce jami’an hukumar ba su kai wani samame a ofishin NLC ba.

A cewar sa, “Hukumar DSS ba ta kai samame ofishin NLC da ke Abuja ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here