Connect with us

Labarai

Za’a ƙara farashin man fetur, saboda tashin dala

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Za a iya cewa har yanzu tsugune ba ta ƙare wa ‘yan Najeriya ba, game da matsalar tattalin arziƙi da suke fuskanta.

Wannan kuwa ya biyo bayan tashin farashin da ake fuskanta na dalar Amurka wanda ke ƙara ta’azzara abubuwa a Najeriya.

Kusan farashin komai a ƙasar ya ta’allaƙa ne da farashin dala, saboda kusan komai shigar mata da shi take daga ƙasashen ƙetare.

Hakan ya haifar da jita-jita cewa farashin man fetur da ake sayarwa a naira 617 a yanzu zai ƙara tashi.

Dalilin da ya sanya ƙungiyar manyan dillalan man fetur na ƙasa wato IPMAN ta mayar da martani kan wannan jita-jita.

KU KUMA KARANTA: Masu sayar da man fetur na arewa sun yi barazanar shiga yajin aiki

Chinedu Okoronkwo shi ne shugaban ƙungiyar na ƙasa ya ce “matuƙar dala za ta tashi farashin man fetur zai tashi shi ma”.

“Ba ma iya samun dala a bankunan kasuwanci kuma idan kaje kasuwar bayan fage farashin ya wuce duk yadda kake zato,” in ji Chinedu.

Shugaban ƙungiyar reshen jihar Kano, Bashir Ɗan Mallam, ya shaida wa BBC cewa “a yanzu farashin mai ya tashi a Legas da wurare da yawa, yanzu fa masu gidajen mai sai dai su haɗa hannu su sayi mota guda”.

“Ta yaya za mu iya tunkarar mutanen Najeriya da wannan tsada, ina ganin sai dai mu rufe gidanjen man, mu zuba wa sarautar Allah ido,” in Bashir Ɗanmalan.

Man da ake saya daga waje zuwa Najeriya ana sayansa ne da dalar Amurka, wadda farashinta ya haura naira 940 a cewar wani ɗan kasuwa da ke Legas a Najeriyar.

Tashinta kuma zai iya haifar da tashin farashin mai wanda shi kuma ake sayar da shi a naira 617, kuma ba a san ko nawa zai iya komawa ba idan ƙarin da ake tsammani ya auku.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed TInubu ne dai ya sanar da cire farashin mai a ƙasar, a ranar da aka rantsar da shi a matsayin shugaba.

Kuma tun bayan nan farashin abubuwa ke ƙara ta’azzara a ƙasar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Amfani da iskar gas na dafa abinci a janareta yana taimakawa masu MSME | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like