Connect with us

Labarai

Za mu sake duba biyan albashin ma’aikatan gwamnati – Tinubu ga shugaban bankin duniya

Published

on

Daga Nusaiba Hussaini

Shugaba Bola Tinubu ya ce ana ci gaba da binciken ƙwaƙwaf na babban bankin Najeriya (CBN).

Shugaban ya kuma ce ana shirin yin garambawul a kan albashin ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Tinubu ya yi magana ne a ranar Juma’a a fadar shugaban ƙasa yayin ganawa da Ajay Banga, shugaban bankin duniya.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi a babban bankin. Za mu yi nazari sosai kan tsarin albashin ma’aikatan gwamnati,” in ji Tinubu a wata sanarwa ɗauke da sa hannun Ajuri Ngelale, mashawarcinsa na musamman kan harkokin yaɗa labarai.

“Ba zan iya yarda da alƙaluman da nake gani ba kuma na taɓa samun irin wannan ƙwarewa a matakin jiha.“Gwamnatin ta zo daidai da sauƙin tsarin kasuwanci a Najeriya. Za mu toshe duk mabuɗin kuɗi, gyare-gyaren za a yi niyya ne a kan yadda muke aiki, canza halaye da kuma daidai da ilmantar da jama’armu. Yana da tsada amma za mu yi. “

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya ta shirya gyaran hanyar jirgin ƙasa na Abuja, zai lanƙwame naira biliyan biyar

A kwanakin baya jaridar TheCable ta ruwaito cewa shugaban ƙasar ya naɗa Jim Obazee, tsohon babban jami’in gudanarwa na hukumar bayar da rahoton kuɗi na Najeriya, domin ya binciki CBN da sauran su.

Tinubu ya kuma ce ya kamata cibiyar Bretton Woods ta kalli ƙasar nan a matsayin mai taka rawa a fagen duniya, ba wai kawai a matsayin ƙasa mai fama da matsalar tattalin arziƙi ba.

“Muna tsaye a matsayin al’umma mai fa’ida kuma mai ilimi, muna neman kawar da hargitsi ta hanyar dabaru. Haɗin gwiwar ku ya yi daidai da neman haɗin gwiwa, kuma tare, za mu ci gaba da amfanar juna wanda zai wadatar da mu duka,” in ji shi.

Shugaban ya yi ƙira da a ƙara tallafi daga bankin duniya domin rage raɗaɗin talauci a ƙasar.

Tinubu ya ce gwamnatinsa ta mayar da hankali ne kan sauye-sauye masu yawa, kamar ƙarfafa gyare-gyare a harkar man fetur, da samar da sauƙin gudanar da kasuwanci, da ba da fifiko kan harkokin tsaro domin bunƙasa kuɗaɗen shiga.

A nasa ɓangaren, Banga ya yabawa Tinubu kan ƙoƙarin da yake yi na magance ƙalubalen tattalin arziƙin ƙasar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Gwamnatin Najeriya ba ta da shirin ƙara haraji – Kwamitin Shugaban ƙasa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Published

on

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

 

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).

“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.

Continue Reading

Labarai

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Published

on

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

 

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.

Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.

Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.

Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:

* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.

* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.

* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.

* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.

* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.

* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.

Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.

Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.

Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.

KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano

Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.

An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.

Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like