Connect with us

Ƙasashen Waje

Za mu nuna wa duniya cewa Isra’ila ta aikata laifukan yaƙi – Erdogan

Published

on

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana cewa ƙasarsa ta soma shirin nuna wa duniya cewa Isra’ila ta aikata laifukan yaƙi, a daidai lokacin da dubban mutane suke gangami da kuma nuna goyon baya ga Falasɗinu.

“A daidai lokacin da muke ɗaga muryoyinmu ga duniya muke shaida musu jin daɗinmu kan cikarmu shekara 100 da zama Jamhuriya a gobe, a yau muna magana kan abin da ke mana ciwo a zukatanmu kan Gaza,” in ji Shugaba Erdogan a lokacin da yake jawabi ga gangamin da ake yi a filin jirgin Ataturk a ranar Asabar.

Hotuna da bidiyo daga filin jirgin sun nuna mutane daga wurare da dama suna ɗauke da tutocin Turkiyya da na Falasɗinu, wasu na saka maka-wuya inda aka rubuta, “Dukkanmu Falasɗinawa ne,” “A kawo ƙarshen kisan kiyashi, a bar yara su rayu” “Sannan a zama murya ga yaran Falasɗinawa.”

“Ya Gaza da ke Falasɗinu take a 1947? Ya take a yau? Isra’ila ta ya kuka je can? Ta ya kuka shiga? Ku ‘yan mamaya ne, ku ƙungiya ce,” in ji Erdogan, inda ya bayyana cewa Turkiyya za ta gabatar da Tel Aviv ga duniya a matsayin wadda ta aikata laifukan yaƙi.

KU KUMA KARANTA: Iran ta gargaɗi Isra’ila kan ci gaba da kai hari kan Falasɗinawa

Ana gudanar da kisan kiyashi mummuna a Gaza, kamar yadda ya bayyana, inda yake ƙara tambaya kan yara da tsofaffi nawa da ba su ji ba su gani ba za a ƙara kashewa kafin a tsagaita wuta.

A yayin da yake caccakar ƙasashen Yamma kan irin goyon bayan da suka nuna wa Isra’ila da kuma yadda suka yi amfani da kafafen watsa labarai domin halatta kisan kiyashin mutanen da ba su da laifi a Gaza, Erdogan ya jaddada cewa goyon bayan Turkiyya ga Falasɗinu inda ya ce: “Isra’ila na bin ƙasashen Yamma bashi amma ba ta bin Turkiyyya. Shi ya sa muke magana ba tare da tsoro ba.”

“Littafin zunubai na ƙasashen Yamma ya sake wuce gona da iri,” kamar yadda ya ƙara da cewa, inda ya ce Isra’ila ba za ta iya aikata irin wannan zaluncin ba tare da taimakon ƙasashen Yamma ba.

‘Ba yaƙi tsakanin tsara ba ne’

Shahararren mawaƙin nan na duniya Yusuf Islam wanda aka fi sani da Cat Stevens shi ma ya yi jawabi a lokacin gangamin goyon bayan Falasɗinawa kan “tayar da bam kan iyalai da ba su ji ba su gani ba, da gidajensu musamman ƙananan yara waɗanda su ne rabin waɗanda aka kashe”.

Ya gode wa Turkiyya kan “tsayawa yadda ya kamata” dangane da halin da ake ciki a Gaza.

“Wannan ba yaƙi bane tsakanin waɗanda ƙarfi ya zo ɗaya. Idan muka kalli irin harin da aka kai a ranar 7 ga watan Oktoba da kuma yadda sojoji suka mayar da martani, ya wuce a yi kwatance,” in ji Islam.

Ya buƙaci ‘yan Isra’ila da su tuna abin da aka ce a cikin Attaurah: Ku tuna asalin saƙon da ubangiji ya aiko muku: Kada ku yi kisa, kada ku yi sata, kada ku nemi kayayyakin maƙwaftanku.’ Waɗannan su ne dokokin da Annabi Musa ya koya wa duniya. Me ya sa ba ku bin su?”

Tsawon makonni uku, Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare ba ƙaƙƙautawa ta sama da ƙasa kan Gaza, inda ta yi wa birnin baki ɗaya ƙawanya da kuma toshe duk wasu hanyoyi da za a shigo da abinci da fetur da magunguna.

Aƙalla Falasɗinawa 7,326 aka kashe a yayin hare-haren, inda kaso 70 cikin 100 mata ne da yara, kamar yadda alƙaluman hukumomi suka tabbatar.

A ranar Juma’a, Isra’ila ta katse hanyoyin sadarwa da na intanet a Gaza da ta mamaye, inda ta hana jama’ar birnin waɗanda ba su da yawa saduwa da sauran jama’ar duniya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like