No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za mu kawo ƙarshen hukunce-hukuncen kotuna masu karo da juna – Ministan Shari’a

Ministan shari’a kuma babban lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen yadda kotunan ke yin hukunce-hukunce masu karo da juna.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Talata a Ilori wajen buɗe taron kwana uku na kawo sauye-sauye a harkokin shari’a a Najeriya.

Ma’aikatar shari’a ta ƙasa tare da taimakon Ƙungiyar Tarayyar Turai ne ta shirya taron.

Mista Fagbemi, ya ce sabon alkalin alkalan Najeriya a shirye yake ya bayar da haɗin kai wajen yin wannan gyara.

Kuma ya ce shugabancin ƙungiyar lauyoyi ta Najeriya, ya nuna cewa lallai akwai buƙatar kawo ƙarshen matsalar.

KU KUMA KARANTA: Kama Mabarata a Najeriya: Wani babban lauya ya maka ministan Abuja a kotu

Fagbemi, ya ce sauye-sauyen da ake matuƙar buƙata a ɓangaren shari’a suna da muhimmanci sosai ga tsari da shirye-shiryen gwamnatin yanzu na bunƙasa Najeriya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...